advanced Search
Dubawa
6190
Ranar Isar da Sako: 2012/05/05
Takaitacciyar Tambaya
don me ake kiran annabi Muhammad (s.a.w) amintacce?
SWALI
don me ake kiran annabi Muhammad (s.a.w) da Muhammad amintacce?
Amsa a Dunkule
Amintacce shi ne kishiyan mayaudari, watau ana nufin mutumin da ba ya yaudarar jama’a, kuma kowa ya natsu da shi ya dogara da shi bisa kyawun dabi’unsa. Idan muka waiga zuwa ga halayen Annabi (s.a.w) ta mu’amala da daidaku da al’umma tun a samartakarsa, zamu ga amana wata dabi’a ce da ta samu gindin zama a gun sa saboda ya Shahara da gaskiya da amana a tsakanin mutane kana kowa ya natsu da shi, wannan ya sa ake kiran sa da “Al’amin”.
Abin da yake da muhimmanci mu fadi a nan shi ne bayan kasantuwar Annabi (s.a.w) aminin wahayin Allah ne, abin dogaro ne a gun Allah (s.a.w) kamar yadda ya kasance a gun jama’a.
A addu’o’i na ziyarar Annabi (s.a.w) kamar yadda aka ruwaito daga Ma’asumai (a.s) sun zo da lafuza Kalmar “Aminullahi” a gurare da dama. Kana dimbin ruwayoyi da suka zo da wannan lakabi suna da damar gaske, wadda hakan zai kara tabbatar da abin da muke zance a kai.
Amsa Dalla-dalla
Amintacce shi ne kishiyan mayaudari, watau ana nufin mutumin da ba ya yaudarar jama’a, kana kowa ya natsu da shi ya dogara da shi bisa kyan dabi’unsa[1]. Idan muka waiga zuwa ga halayen Annabi (s.a.w) wajen mu’amala da daidaku da kuma al’umma tun a samartakarsa,1 zamu ga wata dabi’a ce da ta samu gindin zama a gun sa saboda ya Shahara da gaskiya da amana a tsakanin mutane kana kowa ya natsu da shi, shi ya sa a ke kiransa da “Al’amin”.
An ruwaito cewa wani ayari na fatake da ya bar Makka ya tafi Basara da ke kasar Sham don yin kasuwanci, sun tadda wani fasto na jiran ayarin. Suna isa sai ya tambaye su; A cikin masu aikin hajji na wannan shekara akwai mutanen Makka? Sai suka ce: “Akwai”. Sai ya ce: “To ku tambaya Ahmad bin Abdulmudallib ya bayyana? Domin a wannan watan zai bayyana, kuma shi ne Annabin karshe”. Mai ruwayar ya ce: “Da na dawo Makka sai na tambaya me ya faru”? Sai suka ce: “Muhammad bin Abdullah Al’amin[2] ya yi da’awar Annabta”[3].
Abin da yake da mahimmanci mu fadi a nan shi ne bayan kasantuwar Annabi (s.a.w) aminin wahyin Allah ne, abin dogaro gun Allah (s.a.w) kamar yadda ya kasance a gun jama’a. Wannan shi ne dalilin kiransa da “Al’amin” kamar yadda ya zo a Kur’an da kuma hadisai. Kana Annabi ba ya da bambanci da sauran annabawa, domin duka annabawa amintattu ne na wahayin Allah (s.w.t). Shi ya sa Allah ke fada a kissar Annabi Hudu (a.s) Ya ke cewa: “Isar muku nake da sakonnin Ubangijina kuma ina mai muku nasiha ne amintacce. ”3. Kamar yadda Kur’ani Mai Girma ya kawo a bisa harshen Annabi Nuhu da Annabi Ludu da Annabi Salihu da Annabi Shu’aibu (a.s) kowanne sai da ya cewa jama’arsa: “Hakika ni, manzo ne amintacce”[4].
Akwai gurare da dama a addu’o’in ziyarar Annabi (s.a.w) da Ma’asumai suka ruwaito mukan kira Annabi da Kalmar “Aminulallah”. Daga cikinsu akwai inda muke zantawa da shi a wasu ziyzrce-ziyarce muna cewa “Assalumu alaika ya rasulallah (s.a.w) Muhammadu Aminullahi wa ala rusuliHi wa aza’imi amriHi…”[5]. Ruwayoyi sun yawaita zuwa da wannan a gurare da dama, zamu kawo guri daya don ba da misali:
 An karbo daga Abdullahi bin Jundub yana cewa: Imamu Rida (a.s) ya rubuta wasika zuwa gare ni ya ce: “Bayan haka, hakika Allah Ya aiko Muhammadu (s.a.w) ya kasance Aminin Allah a halittarSa, bayan kauransa sai mu Ahlul baiti muka gaje shi mu ne amintattu na Allah a bayan kasarSa”[6].
 

[1] Almuhaiyir, Rida, Almu’ajam Al’abajadi (Arabi-Farisi) sh4.
[2] Arruwandi, Kudubuddin, Alkhara’ij j1, sh125-126, wal Jawarih, Mu’assatul Imamu ul Mahdi (AJ) Kum, 1409 K.
[3] Al’a’raf: 68.
[4] Ashu’ara: 107,125’143’ 162’ 178.
[5] Ibinkulkwaih Alkummi, Kamiluzziyara’at, sh 201. dabaa’in IntiShara’at murtadyah, Najafui Ashraf,1365,H.
[6] Alkulaini, Muhammad bin yakub, Alkafi, j1, sh223, Darulkutub Al-islamiyah,Tehran, 1365, H.
TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • Da”awar shi”a kan riddar sahabban mazon Allah {s.a.aw} bayan wafatinsa da wacce ma”ana sahabban su ka yi riddar? Shin wannan da”awa za ta iya karbuwa kuwa?.
    12161 Tsohon Kalam 2014/01/27
    samuwar karkata daga nau”in bidi”a da ridda tsakankanin sashen sahabban manzon Allah {s.a.w} bayan wafatinsa. Na farko: daga mahangar littafai na tushe na al”ummar musulmi faruwar hakan wani abu ne da aka sallamawa da babu kokwanto ko shakka ciki sannan kuma sam bai kebantu da littafan shi”a ...
  • Mene ne ma'anar jagorancin malami?
    12834 Sabon Kalam 2012/07/24
    Kalmar Wali da larabci tana da ma'ana guda uku: 1-masoyi, 2-aboki, 3-mataimaki. Bayan haka akwai wasu kalmomi kuma da suke nufin; 1-Salladuwa 2-Jagoranci da shugabanci. "Wilaya" kalma ce da ake amfani da ita da ma'ana biyu a isdilahin fikihu: 1- Wuraren da wanda ...
  • Shin mutum zai iya dawwama; idan haka ne, don me ya sa bai dawwama ba a duniya?
    11634 Sabon Kalam 2012/07/24
    Yana daga abin da yake jan hankli mai kyau a cikin kur’ani mai girma cewa yana ganin mutum wani halitta ne na sama madaukaki mai ‘yanci, kuma wannan jikin nasa ba komai ba ne sai wata sheka ta dan wani lokaci da ruhinsa ya fake a ciki ...
  • Menene hukuncin miji da mata wadanda suke kallon fim din blue fim a tare?
    6979 2018/11/04
    an tambayi daftrorin marja’ai masu alfarma kan tambayar da ka yi kuma ga amsar da suka turo. Ofishin mai girma Ayatullah sayyid Ali Khamna’i (Allah ya tsawaita rayuwarsa): Kalllon finafinai masu tada sha’awa na sa mutun ya karkata zuwa tafarkin shedan na son zuciya kuma yana raunana ...
  • WADAN NE BAITOCI NE ABBAS YAKE RERAWA A LOKACIN DA YA ZO DIBAN RUWA?
    11564 Sirar Manya 2012/07/26
    Mayaka yayin mubaraza a zamanin da su kan yi amfani da wani zaurance (don shaida juna ko ba da sako a tsakaninsu) don haka su kan rera baitotocin waka don samar da karfin gwiwa ga mutanensu da raunana abokan gaba. Imam (a.s) da mutanensa sun yi amfani ...
  • don me ake kiran annabi Muhammad (s.a.w) amintacce?
    6189 تاريخ بزرگان 2019/06/12
    Amintacce shi ne kishiyan mayaudari, watau ana nufin mutumin da ba ya yaudarar jama’a, kuma kowa ya natsu da shi ya dogara da shi bisa kyawun dabi’unsa. Idan muka waiga zuwa ga halayen Annabi (s.a.w) ta mu’amala da daidaku da al’umma tun a samartakarsa, zamu ga amana ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    14051 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...
  • Wasu irin hadisai ne suka zo a kan Hukuncin dan zina?
    14544 Dirayar Hadisi 2012/07/25
    Ruwayoyi na musulunci daga annabi (saw) sun yi magana da bayyana hukunce hukuncen dan zina, za mu kawo irin babobinsu Gadon dan zina;- Babin cewa dan zina, shi wanda ya yi zinar ba zai gaje shi ba, da ita mazinaciyar, ko wanda ...
  • Ta wace hanya za mu iya kare kanmu daga kanbun baka?
    26372 Tafsiri 2017/05/20
    Kanbun baka na da tasiri a ruhin mutun wanda babu wani dalili da za a iya kore samuwar sa da shi, ballantana ma an ga faruwar abubuwa masu yawa da suka tabbatar da samuwar kanbun baka ko maita. Marigayi shekh Abbas Kummi ya yi wasici da a ...
  • Shin zai iya yuwuwa a kai ga martabar ubangijintaka?
    8568 Irfanin Nazari 2012/07/25
    Makamin matsayin ubangijintaka yana da matakai da marhaloli mabambanta, kuma don a samu wannan amsar dole ne a ga dukkan martabobi da ma’anonin baki daya. Idan abin da ake nufi da kai wa matakin ubangijintaka shi ne zatin mutum ta canja da sauyawar abin halitta ya koma ...

Mafi Dubawa