advanced Search
Dubawa
8177
Ranar Isar da Sako: 2012/03/04
Takaitacciyar Tambaya
Duk da kasancewar Zahara (a.s) ta bar wannan Duniyar a lokacin da take da Karancin Shekaru ne, ba ta yi tsawon Rayuwa ba, a Bangare daya ke nan, a Daya bangaren kuma Hadisan da aka karbo daga wajenta ba su da yawa, gashi ta yi shekaru goma na Yaranta, to, ta yaya za a iya suranta cewa ta kai irin wannan matsayin da irin wannan darajar? A takaice dai mene ne ya taimaka mata, Alhali tana yarinya mai shekaru goma sha takwas, ta kai matsayin da yake dai dai da na Annabawa ne, wasu irin kamala take da su har ta cancanci wannan matsayin? Don Allah a bamu amsa mai gamsarwa.
SWALI
Duk da kasancewar Zahara (a.s) ta bar wannan Duniyar a lokacin da take da Karancin Shekaru ne, ba ta yi tsawon Rayuwa ba, a Bangare daya ke nan, a Daya bangaren kuma Hadisan da aka karbo daga wajenta ba su da yawa, gashi ta yi shekaru goma na Yaranta, to, ta yaya za a iya suranta cewa ta kai irin wannan matsayin da irin wannan darajar? A takaice dai mene ne ya taimaka mata, Alhali tana yarinya mai shekaru goma sha takwas, ta kai matsayin da yake dai dai da na Annabawa ne, wasu irin kamala take da su har ta cancanci wannan matsayin? Don Allah a bamu amsa mai gamsarwa.
Amsa a Dunkule

 Ba shakka cewa Kur’ani ya bayyana a Fili cewa Annabi Isa (a.s) an ba shi Matsayi mai Girma Alhali ma yana cikin Tsumman Goyo: ’sai Ta yi nuni a gare shi sai sukace ta yaya zamu yi Magana da wanda yake cikin Tsumma, sai ya ce ni Bawan Allah ne ya bani Littafi kuma ya sanyani Annabi kuma ya sanya ni mai Albarka a duk inda nake kuma ya yi mun wasiyya da Salla da Zakka matukar ina Raye” [1]

 Haka ma a wani wuri a cikin Kur’ani zamu ga Fadar Allah Madaukaki inda ya ce: Kuma zai yi Magana da Mutane Alhali yana cikin Zanin Goyo da kuma Lokacin da yake Dattijo kuma zai zamo a cikin Salihai”[2]

 Har ma Kur’ani ya yi Bayani balo balo a game da al’amarin Annabi yahaya (a.s) a inda Allah Azza wa Jalla ya ce: ya kai Yahaya ka riki Littafin nan da Karfi kuma mun ba shi Hukunci tun Yana Dan Yaro”[3]

 Daga wadannnan Bayanan za a Fahimci cewa babu wani abin Mamaki game da samun Matsayi mai Daraja tun a Farkon Rayuwa, kai, tun A Ranakun farko ma, ko kuma a shekarun farko, kamar al ‘amarin Annabi yahaya (a.s), to, idan muka Tafiyar da wannan Ka’idar ga Shugaban Matan Halittu, wannan Maccen, Mutumiyar Allah zamu ga babu wani Rudewa ko Nisantarwa da zamu hadu da su game da samun da Sayyida Zahara ta yi ga Mukami mai daraja da daukaka, ta yanda a dalilin takawarta da tsantsenin ta samu matsayi irin na Annabawa, amma dai tabbas ita ba Annabiya ba ce, wannan matsayin babu wani mutum mai Adalci, mai girmama Kur’ani wanda ya yi imani da wajabcin jagorancin Kur’ani, da zai yi Shakkar samuwarsa gare ta.

 Ta yanda Kur’ani ya fada a fili a cikin ayar tsarkakewa cewa nufi ne na Allah, na tsarin halittar samuwa, ya nufi tsarkake Ahlul Baiti (a.s) a cikin su kuma akwai Zahara (a.s) daga barin dukkan Datti da Dauda, wanda kuma ita ce Hususiyyar Annabawa, wacce da ita ce suka samu Makami, na Annabci suka zamo Gaskatawa ne ga Fadar Allah madaukaki: Allah shi ne ya san inda zai Sanya Sakonsa”[4] sannan kuma Allah Madaukaki ya fada a cikin Littafinsa mai gima: Iyaka kawai Allah yana nufin ya Tafiyar da Dauda ne ga barin ku Ahlul Baiti kuma ya Tsarkake ku Iyakacin Tsarkakewa”[5]

 Kuma Dukkan Musulmi masu Tafsiri na dukkan Mazhabobi da Dariku sun yi Ijma’i a kan cewa wannan Aya ta Kunshi Sayyidah Zahara (a.s) to, shin akwai wani Matsayi da yake a saman wannan?

 Amma game da Abubuwan da suke Sabbaba samun irin wannan Matsayin, Wasunsu daga Mutum ne shi kansa, wasu kuma daga Tarbiyya ne, wani abun kuma wanda shi yafi Muhimmanci shi ne Ludufin Allah.

 To, amma babu lokacin kawo dukkan wadannan sharhohin a nan.

 za a iya nemansu a mahallinsu.

 Wasu binciken da suke da alaka da wannan bayanin:[6]

  • Matsayin Imaman Shi’a idan an Kwatanta da Matsayin Annabawa 9198 (lambardandalin: 9188).
  • Ma’anar Hadisin da ke cewa ba domin Fatima ba da …. 13495 (lambar dandalin: 13230).
  • Bangarori na matsayin Fatimatuz Zahara (a.s), 2837 (lambar dandalin: 3348).

 

 


[1] Maryam 29-31

[2] Ali imran 46

[3] Maryam12

[4] An’am 124

[5] Ahzab 33

[6]

 

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • Da”awar shi”a kan riddar sahabban mazon Allah {s.a.aw} bayan wafatinsa da wacce ma”ana sahabban su ka yi riddar? Shin wannan da”awa za ta iya karbuwa kuwa?.
    12161 Tsohon Kalam 2014/01/27
    samuwar karkata daga nau”in bidi”a da ridda tsakankanin sashen sahabban manzon Allah {s.a.w} bayan wafatinsa. Na farko: daga mahangar littafai na tushe na al”ummar musulmi faruwar hakan wani abu ne da aka sallamawa da babu kokwanto ko shakka ciki sannan kuma sam bai kebantu da littafan shi”a ...
  • Mene ne ma'anar jagorancin malami?
    12834 Sabon Kalam 2012/07/24
    Kalmar Wali da larabci tana da ma'ana guda uku: 1-masoyi, 2-aboki, 3-mataimaki. Bayan haka akwai wasu kalmomi kuma da suke nufin; 1-Salladuwa 2-Jagoranci da shugabanci. "Wilaya" kalma ce da ake amfani da ita da ma'ana biyu a isdilahin fikihu: 1- Wuraren da wanda ...
  • Shin mutum zai iya dawwama; idan haka ne, don me ya sa bai dawwama ba a duniya?
    11634 Sabon Kalam 2012/07/24
    Yana daga abin da yake jan hankli mai kyau a cikin kur’ani mai girma cewa yana ganin mutum wani halitta ne na sama madaukaki mai ‘yanci, kuma wannan jikin nasa ba komai ba ne sai wata sheka ta dan wani lokaci da ruhinsa ya fake a ciki ...
  • Menene hukuncin miji da mata wadanda suke kallon fim din blue fim a tare?
    6979 2018/11/04
    an tambayi daftrorin marja’ai masu alfarma kan tambayar da ka yi kuma ga amsar da suka turo. Ofishin mai girma Ayatullah sayyid Ali Khamna’i (Allah ya tsawaita rayuwarsa): Kalllon finafinai masu tada sha’awa na sa mutun ya karkata zuwa tafarkin shedan na son zuciya kuma yana raunana ...
  • WADAN NE BAITOCI NE ABBAS YAKE RERAWA A LOKACIN DA YA ZO DIBAN RUWA?
    11564 Sirar Manya 2012/07/26
    Mayaka yayin mubaraza a zamanin da su kan yi amfani da wani zaurance (don shaida juna ko ba da sako a tsakaninsu) don haka su kan rera baitotocin waka don samar da karfin gwiwa ga mutanensu da raunana abokan gaba. Imam (a.s) da mutanensa sun yi amfani ...
  • don me ake kiran annabi Muhammad (s.a.w) amintacce?
    6189 تاريخ بزرگان 2019/06/12
    Amintacce shi ne kishiyan mayaudari, watau ana nufin mutumin da ba ya yaudarar jama’a, kuma kowa ya natsu da shi ya dogara da shi bisa kyawun dabi’unsa. Idan muka waiga zuwa ga halayen Annabi (s.a.w) ta mu’amala da daidaku da al’umma tun a samartakarsa, zamu ga amana ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    14051 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...
  • Wasu irin hadisai ne suka zo a kan Hukuncin dan zina?
    14544 Dirayar Hadisi 2012/07/25
    Ruwayoyi na musulunci daga annabi (saw) sun yi magana da bayyana hukunce hukuncen dan zina, za mu kawo irin babobinsu Gadon dan zina;- Babin cewa dan zina, shi wanda ya yi zinar ba zai gaje shi ba, da ita mazinaciyar, ko wanda ...
  • Ta wace hanya za mu iya kare kanmu daga kanbun baka?
    26372 Tafsiri 2017/05/20
    Kanbun baka na da tasiri a ruhin mutun wanda babu wani dalili da za a iya kore samuwar sa da shi, ballantana ma an ga faruwar abubuwa masu yawa da suka tabbatar da samuwar kanbun baka ko maita. Marigayi shekh Abbas Kummi ya yi wasici da a ...
  • Shin zai iya yuwuwa a kai ga martabar ubangijintaka?
    8568 Irfanin Nazari 2012/07/25
    Makamin matsayin ubangijintaka yana da matakai da marhaloli mabambanta, kuma don a samu wannan amsar dole ne a ga dukkan martabobi da ma’anonin baki daya. Idan abin da ake nufi da kai wa matakin ubangijintaka shi ne zatin mutum ta canja da sauyawar abin halitta ya koma ...

Mafi Dubawa