advanced Search
Dubawa
24740
Ranar Isar da Sako: 2006/05/22
Takaitacciyar Tambaya
iyakokin daular musulunci zuwa ina ne a fikirar siyasar musulunci?
SWALI
iyakokin daular musulunci zuwa ina ne a fikirar siyasar musulunci?
Amsa a Dunkule

Musulunci yana da kalmomi da suka hada da "kasa" da kuma "yanki" da "al'umma. Kasa a tunanin fikirar musulunci wuri ne guda daya, kuma dukkan iyakokin da ake da su ba su da wani tasiri wurin rusa kasancewar kasar musulunci da musulmi abu guda ne. kuma wannan kasa a bisa koyarwar musulunci dole ne ta kasance karkashin jagorancin shugaba daya ma'asumi (a.s), kuma wannan shi ne babban buri da hadafin hukumar Imam Mahadi (a.s).

A lokacin boyuwr Imam Mahadi (a.s) idan an samu damar kafa wannan kasa ta musulunci dunkulalla guda daya kuma aka samu maslahar musulunci wurin tafiyar da wadannan kasashe a matsayin kasa daya, to ya hau kan malami ya tafiyar da ita a yadda take dunkulalla.

Kuma idan wani yanki ne kawai aka samu damar tafiayarwa ta hannun malami to bisa maslahar musulunci da ta dace, haka nan dai ya hau kan malami ya kafa hukuma bisa wannan yankin. Don haka ne bisa asasin tsarin siyasar musulunci kasa dukkanta abu guda ne.

Amma kuma idan ya kasance kasashe a rarrabe suke ko a yanayin garuruwa ne, to bisa maslaha ya kasance wani nauyi na tilas da ya hau kan malami ya tafiyar da wannan yankin bisa dogaro da siyasar da take gudana.

Amsa Dalla-dalla

A yau a bisa taswirar siyasar wannan zamani kasashe sun rarrabu gida-gida, kuma sun sanya musu wasu iyakoki da suka kafa dauloli daban-daban masu bambanta da juna, kuma kowane wuri yana da tasa hukumar. Wadanda suke rayuwa a wannan yankunan suan da zama ne a matsayin 'yan kasa[1], saura kuwa 'yan waje[2] (wadanda ba 'yan kasa ba), hukunce-hukunce wasu sun shafi 'yan kasa ne, wasu kuwa sun shafi 'yan waje ne.

Shin wadannan dokokin suna da wata kima da ake la'akari da ita, to yaya suke ne a bisa mahangar musulunci?

A amsar wannan tambayar muna iya cewa: Musulunci yana ganin kansa a matsayin addinin duk duniya, kuma duk duniya yana ganin kasarta ne kuma dole ne a karbe shi a nan. Kuma duk inda aka samu mafi yawan mutanen wurin musulmi ne, to ana kiran wannan wurin kasar musulunci, daya bangaren kuwa wanda kafirai suak fi yawa ana kiran sa kasar kafirci. Don haka babu wata iyaka a musulunci sai iyakar akida, kuma akida ce kawai take da iyaka a bisa tsarin siyasar musulunci, kuma wannan shi ne musulunci kawai.

"Addini a wurin Allah shi ne musulunci"[3], musulunci yana da ma'anar doron kasa maimakon kasa[4], ya kawo ma'anar al'umma ne maimakon 'yan kasa[5]. Wato musulunci bai yarda da bambanci tsakanin al'ummu da kasa da mutane ba, abin da ya yarda da shi kawai shi ne akida.

Kasar musulunci abu guda ne, kuma wannan iyakokin ba su da wani tasiri a cikin kadaitakar kasar musulunci.

kuma wannan kasa a bisa koyarwar musulunci dole ne ta kasance karkashin jagorancin shugaba daya ma'asumi (a.s), kuma wannan shi ne babban buri da hadafin hukumar Imam Mahadi (a.s).

A lokacin boyuwr Imam Mahadi (a.s) idan an samu damar kafa wannan kasa ta musulunci dunkulalla guda daya kuma aka samu maslahar musulunci wurin tafiyar da wadannan kasashe a matsayin kasa daya, to ya hau kan malami ya tafiyar da ita a yadda take dunkulalla.

Kuma idan wani yanki ne kawai aka samu damar tafiayarwa ta hannun malami to bisa maslahar musulunci da ta dace, haka nan dai ya hau kan malami ya kafa hukuma bisa wannan yankin. Don haka ne bisa asasin tsarin siyasar musulunci kasa dukkanta abu guda ne.

Amma kuma idan ya kasance kasashe a rarrabe suke ko a yanayin garuruwa ne, to bisa maslaha ya kasance wani nauyi na tilas da ya hau kan malami ya tafiyar da wannan yankin bisa dogaro da siyasar da take gudana.

 

Karin bayani:

1. Mahdi Hadawi Tehrani, Wilayat wa Diyanat, Mu'assar Al'adun Khaneye Khirad, Kum, bugu na biyu, 1380.

 


[1] Citizen.

[2] Foreigner.

[3] Aali Imran: 19.

[4] country.

[5] Nation.

 

TARJAMA YA JAWABU KATIKA LUGHA NYENGINE
Mahanga
Idadi ya maoni 0
Tafadhali ingiza thamani
Imel : Yourname@YourDomane.ext
Tafadhali ingiza thamani
Tafadhali ingiza thamani

MPANGILIO WA KIMAUDHUI

Tambayoyi Masu Fadowa

  • Da”awar shi”a kan riddar sahabban mazon Allah {s.a.aw} bayan wafatinsa da wacce ma”ana sahabban su ka yi riddar? Shin wannan da”awa za ta iya karbuwa kuwa?.
    12161 Tsohon Kalam 2014/01/27
    samuwar karkata daga nau”in bidi”a da ridda tsakankanin sashen sahabban manzon Allah {s.a.w} bayan wafatinsa. Na farko: daga mahangar littafai na tushe na al”ummar musulmi faruwar hakan wani abu ne da aka sallamawa da babu kokwanto ko shakka ciki sannan kuma sam bai kebantu da littafan shi”a ...
  • Mene ne ma'anar jagorancin malami?
    12834 Sabon Kalam 2012/07/24
    Kalmar Wali da larabci tana da ma'ana guda uku: 1-masoyi, 2-aboki, 3-mataimaki. Bayan haka akwai wasu kalmomi kuma da suke nufin; 1-Salladuwa 2-Jagoranci da shugabanci. "Wilaya" kalma ce da ake amfani da ita da ma'ana biyu a isdilahin fikihu: 1- Wuraren da wanda ...
  • Shin mutum zai iya dawwama; idan haka ne, don me ya sa bai dawwama ba a duniya?
    11634 Sabon Kalam 2012/07/24
    Yana daga abin da yake jan hankli mai kyau a cikin kur’ani mai girma cewa yana ganin mutum wani halitta ne na sama madaukaki mai ‘yanci, kuma wannan jikin nasa ba komai ba ne sai wata sheka ta dan wani lokaci da ruhinsa ya fake a ciki ...
  • Menene hukuncin miji da mata wadanda suke kallon fim din blue fim a tare?
    6979 2018/11/04
    an tambayi daftrorin marja’ai masu alfarma kan tambayar da ka yi kuma ga amsar da suka turo. Ofishin mai girma Ayatullah sayyid Ali Khamna’i (Allah ya tsawaita rayuwarsa): Kalllon finafinai masu tada sha’awa na sa mutun ya karkata zuwa tafarkin shedan na son zuciya kuma yana raunana ...
  • WADAN NE BAITOCI NE ABBAS YAKE RERAWA A LOKACIN DA YA ZO DIBAN RUWA?
    11564 Sirar Manya 2012/07/26
    Mayaka yayin mubaraza a zamanin da su kan yi amfani da wani zaurance (don shaida juna ko ba da sako a tsakaninsu) don haka su kan rera baitotocin waka don samar da karfin gwiwa ga mutanensu da raunana abokan gaba. Imam (a.s) da mutanensa sun yi amfani ...
  • don me ake kiran annabi Muhammad (s.a.w) amintacce?
    6189 تاريخ بزرگان 2019/06/12
    Amintacce shi ne kishiyan mayaudari, watau ana nufin mutumin da ba ya yaudarar jama’a, kuma kowa ya natsu da shi ya dogara da shi bisa kyawun dabi’unsa. Idan muka waiga zuwa ga halayen Annabi (s.a.w) ta mu’amala da daidaku da al’umma tun a samartakarsa, zamu ga amana ...
  • Menene hukunchi namijin da ba ya iya biyawa matarsa hakkokinta?
    14051 2019/06/16
    dawwamar rayuwar aure da karfafarta ya dogara da soyayya da kauna da fuskantar juna da girmama juna. Domin iyali su samu tsayuwa da dawwama Addini Muslunci ya sanya hakkoki ga kowanne dayansu ya kuma ayyana musu wajibai a kansu, duk sa”ilin da aka ce akwai hakkoki to ...
  • Wasu irin hadisai ne suka zo a kan Hukuncin dan zina?
    14544 Dirayar Hadisi 2012/07/25
    Ruwayoyi na musulunci daga annabi (saw) sun yi magana da bayyana hukunce hukuncen dan zina, za mu kawo irin babobinsu Gadon dan zina;- Babin cewa dan zina, shi wanda ya yi zinar ba zai gaje shi ba, da ita mazinaciyar, ko wanda ...
  • Ta wace hanya za mu iya kare kanmu daga kanbun baka?
    26372 Tafsiri 2017/05/20
    Kanbun baka na da tasiri a ruhin mutun wanda babu wani dalili da za a iya kore samuwar sa da shi, ballantana ma an ga faruwar abubuwa masu yawa da suka tabbatar da samuwar kanbun baka ko maita. Marigayi shekh Abbas Kummi ya yi wasici da a ...
  • Shin zai iya yuwuwa a kai ga martabar ubangijintaka?
    8568 Irfanin Nazari 2012/07/25
    Makamin matsayin ubangijintaka yana da matakai da marhaloli mabambanta, kuma don a samu wannan amsar dole ne a ga dukkan martabobi da ma’anonin baki daya. Idan abin da ake nufi da kai wa matakin ubangijintaka shi ne zatin mutum ta canja da sauyawar abin halitta ya koma ...

Mafi Dubawa